Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya baiwa alhazan jihar Kaduna da ke gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026 a ƙasar Saudiyya kyautar Riyal 300 na Saudiyya ga kowane mahajjaci yayin da ya kai ziyara tantunansu da ke Mina.
A cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Ibraheem Musa ya fitar, ya bayyana cewa kowane mahajjaci zai karɓi kimanin Naira dubu ɗari da goma sha huɗu (N114,000) bisa la’akari da canjin kuɗi na yanzu.
Gwamna Uba Sani ya kai ziyarar ne domin duba yanayin alhazan jihar Kaduna tare da tabbatar da jin daɗinsu yayin gudanar da ibadar Hajji. A yayin ziyarar, ya nuna matuƙar farin cikinsa bisa yadda aka gudanar da aikin Hajjin bana cikin tsari da lumana, tare da yaba wa alhazan jihar saboda kyakkyawan ɗabi’a, biyayya da kuma jajircewarsu wajen gudanar da ibadunsu yadda ya kamata.
Gwamnan ya kuma yaba wa Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna da Kwamitin Tawagar Hajjin Jihar Kaduna saboda ƙoƙarin da suka yi wajen tabbatar da cewa alhazan sun samu kulawa mai kyau tun daga fara tafiya zuwa ƙasar Saudiyya har zuwa lokacin gudanar da muhimman ayyukan Hajji.
Sanata Uba Sani ya yi musamman yabo ga Kwamitin Tawagar Hajjin Jihar Kaduna ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abubakar Mustapha, inda ya ce kwamitin ya nuna ƙwarewa da sadaukarwa wajen gudanar da ayyukansa, lamarin da ya taimaka wajen samun nasarar gudanar da aikin Hajjin bana ba tare da manyan matsaloli ba.
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ɗauki matakai da dama tare da samar da dukkanin abubuwan da suka dace domin tabbatar da cewa alhazan Kaduna sun gudanar da ibadarsu cikin sauƙi da kwanciyar hankali. Ya kuma nemi afuwar alhazan kan duk wasu ƙananan matsaloli ko tsaiko da suka iya fuskanta yayin aikin Hajjin, yana mai jaddada cewa irin waɗannan matsaloli ba da gangan suka faru ba, sai dai wasu ƙalubale ne da kan iya tasowa a irin wannan babban taro na duniya.
Haka kuma, Gwamna Uba Sani ya yi kira ga alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba. Ya bayyana cewa babu wata al’umma da za ta samu ci gaba mai ɗorewa idan babu zaman lafiya da kwanciyar hankali. A cewarsa, zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaban tattalin arziki, ilimi, kiwon lafiya da sauran fannoni na rayuwar al’umma.
Ya kuma roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya shiryar da duk masu haddasa rikice-rikice da tashin hankali a cikin al’umma, tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan sassan ƙasar nan.
Tun da farko, Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu Sani Abubakar, ya gode wa Gwamna Uba Sani bisa irin goyon baya da kulawar da yake baiwa hukumar da kuma alhazan jihar. Ya ce gwamnan ya kawo sauye-sauye masu yawa wajen inganta walwala da jin daɗin alhazan, wanda hakan ya taimaka wajen samun nasarar gudanar da aikin Hajjin bana.
A nasa jawabin godiya, Babban Mai Binciken Kuɗaɗen Jihar Kaduna (Auditor General), Alhaji Abubakar Abdullahi, ya bayyana cewa Gwamna Uba Sani shi ne gwamnan jihar Kaduna na farko tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a shekarar 1999 da ya kai ziyara kai tsaye ga alhazan jihar a cikin tantunansu yayin gudanar da aikin Hajji.
Ya ce wannan mataki ya nuna irin kulawar da gwamnan yake da ita ga al’ummar jihar, musamman ma wadanda suke gudanar da wannan muhimmin rukuni na addinin Musulunci. Alhaji Abubakar Abdullahi ya ƙara da cewa ziyarar da kuma kyautar da aka baiwa alhazan za su kasance abin tunawa na musamman ga mahajjatan Kaduna, tare da ƙarfafa musu gwiwa wajen ci gaba da yi wa jihar da ƙasa baki ɗaya addu’o’in alheri.
Alhazan jihar Kaduna sun nuna farin ciki da jin daɗinsu kan wannan karamci da gwamnan ya nuna musu, inda suka yi masa addu’ar Allah Ya ƙara masa lafiya, hikima da nasara wajen jagorantar jihar Kaduna zuwa ga ci gaba da wadata.
