Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayar da umarnin gaggauta ci gaba da kuma kammala aikin titin Nnamdi Azikiwe Western Bypass cikin hanzari, bayan yawaitar hatsarori masu muni da ke haddasa asarar rayuka a kan titin.
An bayar da wannan umarni ne bayan wani taron gaggawa da gwamnan ya kira, wanda ya haɗa masu ruwa da tsaki domin tattauna hanyoyin magance yawan hatsarorin da ke faruwa a kan titin mai tsawon kilomita 21.5 daga Command Junction zuwa Mando Roundabout.
Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu, Ahmed Maiyaki, ya bayyana cewa gwamnan na cikin matuƙar damuwa kan yadda ake rasa rayuka sakamakon waɗannan hatsarori. Ya ce wannan lamari ba abin amincewa ba ne, yana mai jaddada cewa babu wani ci gaba da ya kamata ya jawo asarar rayukan jama’a.
Maiyaki ya bayyana cewa duk da cewa an kammala kusan kilomita 19 na aikin titin, gwamnan ya bayar da umarnin a kammala aikin kafin wa’adin Disamba 2026 da aka sanya a baya. Ya ce hakan na daga cikin matakan gaggawa domin rage hatsarori da kuma inganta zirga-zirga.
Ya kuma ƙara da cewa an kafa wani kwamiti na haɗin gwiwa daga hukumomi daban-daban domin sa ido kan aikin da kuma tabbatar da bin ƙa’idojin tsaro, musamman a lokacin damina inda hanyoyi kan lalace kuma gani ya kan ragu.
Kwamishinan ya kuma nuna cewa rashin bin dokokin hanya daga wasu masu amfani da titin na daga cikin abubuwan da ke haddasa hatsarorin. Ya ambaci gudu fiye da kima, tukin ganganci, da rashin kiyaye dokokin hanya a matsayin manyan matsaloli. Saboda haka, gwamnati na shirin ƙarfafa wayar da kan jama’a kan muhimmancin kiyaye dokokin tuki.
Haka kuma, gwamnati za ta yi aiki tare da hukumomin tsaro domin tabbatar da bin dokokin hanya, ciki har da sanya ido kan direbobin motocin haya, kayyade gudu, da kuma sanya alamun gargadi a wuraren da suka dace.
Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun nuna goyon bayansu ga wannan mataki. ‘Yan kwangila sun yi alkawarin ƙara ƙaimi wajen aikin domin kammala shi cikin lokaci, yayin da ƙungiyoyin direbobi suka yi alƙawarin wayar da kan mambobinsu kan tuki cikin aminci.
Titin Nnamdi Azikiwe Western Bypass na daga cikin muhimman ayyukan da aka tsara domin rage cunkoso a cikin birnin Kaduna da samar da wata hanya ta daban ga masu ababen hawa. Sai dai yawaitar hatsarori a baya-bayan nan ya jawo damuwa, wanda ya sa gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa.
Matakin da Gwamna Uba Sani ya ɗauka na nuna ƙudirin gwamnatinsa wajen kare rayukan jama’a da tabbatar da cewa ayyukan ci gaba suna amfani ga al’umma ba tare da haifar da illa ba. Yanzu dai jama’a na fatan cewa waɗannan matakai za su dawo da tsaro da kwanciyar hankali a kan titin.
