Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya samu lambar yabo ta Gwamnan Shekara daga jaridar Leadership, sakamakon abin da masu shirya bikin suka bayyana a matsayin salon shugabanci nagari mai cike da adalci da haɗin kai.
An ba shi lambar yabon ne a wani gagarumin biki da aka gudanar a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Ƙasa (International Conference Centre) da ke Abuja, inda shugabannin siyasa, masana harkokin mulki, ‘yan jarida da masu ruwa da tsaki suka hallara domin karrama fitattun jagorori a Najeriya.
Masu shirya bikin sun bayyana cewa karramawar ta nuna irin tsarin mulkin gwamnan wanda ke inganta zaman lafiya tsakanin addinai da kabilu, tare da tabbatar da cewa ana rarraba ayyukan ci gaba a dukkanin yankuna uku na sanatan jihar.
Sun ƙara da cewa gwamnatin na mayar da hankali wajen kai ayyukan more rayuwa zuwa wuraren karkara da a baya ba su da isasshen ci gaba, domin rage gibin da ke tsakanin birane da ƙauyuka.
Makonnin da suka gabata kafin karɓar lambar yabon, gwamnan ya ƙaddamar da manyan ayyukan hanyoyi a sassa daban-daban na jihar domin sauƙaƙa zirga-zirga, inganta tsaro da bunƙasa tattalin arziki.
A Yanki na Ɗaya, ayyukan sun haɗa da hanyar Durum zuwa Kuruntumawa a Ƙaramar Hukumar Makarfi, hanyar Magajiya zuwa Albarkawa da kuma hanyar Audi zuwa Kako a Zariya. Mazauna yankunan sun ce hanyoyin za su taimaka wajen sauƙaƙa kai kayan amfanin gona kasuwa tare da rage kuɗin sufuri.
A Yanki na Tsakiya, gwamnan ya buɗe hanyar kilomita 35 daga Gwaraji a Igabi zuwa Maraban Kajuru. Jami’ai sun bayyana wannan a matsayin mafi tsawon aikin hanya da aka yi a jihar cikin shekaru ashirin da suka gabata. Ana sa ran hanyar za ta inganta haɗin kai tsakanin al’ummomi tare da sauƙaƙa ayyukan tsaro a yankunan da ke da wahalar shiga.
A Yanki na Uku, gwamnan ya kuma ƙaddamar da hanyar kilomita 32 daga Madauchi zuwa Madakiya, wadda ake sa ran za ta ƙara habaka kasuwanci da harkokin noma a kudancin jihar.
Baya ga hanyoyi, gwamnatin ta aiwatar da shirye-shiryen ci gaban jama’a da dama. An gyara asibitoci da cibiyoyin kula da lafiya na matakin farko tare da samar da kayan aiki na zamani domin inganta kula da lafiya musamman a yankunan karkara.
Haka kuma an gina sabbin makarantu da karin azuzuwa domin rage cunkoso a ajujuwa da kuma inganta yanayin karatu ga ɗalibai. Jami’an ilimi sun ce wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin rage yawan yara marasa zuwa makaranta a jihar.
Bugu da ƙari, an ƙaddamar da shirye-shiryen tallafawa matasa da mata ta hanyar horas da sana’o’i, tallafin kananan sana’o’i da samar da ayyukan yi. Wadanda suka amfana sun bayyana cewa sun samu ci gaba a rayuwarsu ta hanyar horo da tallafin jari.
Jaridar Leadership ta ce lambar yabon ta girmama tsarin mulkin gwamnan da ya fi mayar da hankali ga jama’a, tare da tabbatar da cewa ayyukan ci gaba sun kai ga al’ummomi a birane da karkara ba tare da la’akari da kabila ko addini ba.
Masu lura da al’amuran siyasa sun ce wannan karramawa na nuna muhimmancin shugabanci mai haɗa kai a Najeriya, inda a yanzu ake auna ci gaba ba kawai da manyan ayyuka ba, har ma da yadda talakawa ke amfana da manufofin gwamnati.
Da yake karɓar lambar yabon, Gwamna Uba Sani ya sadaukar da ita ga al’ummar Jihar Kaduna tare da jaddada kudurinsa na ci gaba da samar da ayyukan more rayuwa, ayyukan jin ƙai da damar tattalin arziki ga kowa da kowa.
