Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya karɓi ragowar masu ibada tamanin da tara (89) da aka sace daga wani coci da ke Kurmin Wali, a Ƙaramar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna, bayan nasarar kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane.
Masu ibadar sun faɗa hannun ’yan bindiga ne a lokacin da suke tsaka da gudanar da ibada a cocin, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici da tashin hankali. Bayan sace su, ’yan bindigar sun rike su a cikin daji na tsawon lokaci kafin daga bisani jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki suka samu nasarar ceto su lafiya.
Da yake karɓar su a Fadar Gwamnatin Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya bayyana matuƙar godiyarsa ga jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji, ’yan sanda, DSS da sauran hukumomin tsaro, bisa jajircewa da sadaukarwa da suka nuna har aka samu nasarar ceto mutanen. Gwamnan ya ce aikin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da hukumomin tsaro shi ne ginshiƙin samun nasarori irin wannan, yana mai jaddada cewa gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Sanata Uba Sani ya kuma sake tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatinsa ta kuduri aniyar inganta tsaro a faɗin Kaduna, musamman a yankunan karkara da suka fi fuskantar barazanar hare-haren ’yan bindiga. Ya ce an riga an ɗauki sabbin matakai na ƙarfafa tsaro, haɗa bayanan sirri, da kuma tallafa wa jami’an tsaro da kayan aiki da dabaru na zamani.
Gwamnan ya yi kira ga mutanen Kurmin Wali da sauran al’ummomin jihar da su ci gaba da kasancewa masu natsuwa da taka-tsantsan, tare da bai wa hukumomin tsaro cikakken haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai a kan lokaci. A cewarsa, haɗin kai tsakanin jama’a da jami’an tsaro na da matuƙar muhimmanci wajen dakile ayyukan miyagu.
A matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnati na farfaɗo da yankin, Gwamna Uba Sani ya sake jaddada alkawarin gwamnatinsa na gina hanya da asibiti a Kurmin Wali domin sauƙaƙa zirga-zirga da inganta kiwon lafiya ga al’ummar yankin. Ya bayyana cewa irin waɗannan ayyukan raya ƙasa za su taimaka wajen rage matsalolin tsaro ta hanyar samar da cigaba da walwala ga jama’a.
Da take magana a madadin waɗanda aka ceto, Misis Rebecca Hosea ta nuna godiya ga gwamnan bisa ƙoƙarin da ya yi ba dare ba rana domin ganin sun samu ’yanci. Ta ce sun sha wahala a lokacin da suke tsare, amma sun yi imani da cewa gwamnati ba za ta manta da su ba. Ta kuma gode wa jami’an tsaro da duk wanda ya taka rawa wajen kubutar da su.
Haka zalika, Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen Jihar Kaduna, Reverend Caleb Ma’aji, ya yaba da salon shugabancin Gwamna Uba Sani, yana mai bayyana shi a matsayin shugaba mai haɗa kai da saurin ɗaukar mataki wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Ya ƙarfafa gwamnan da ya ci gaba da wannan ƙwazo ba tare da gajiya ba.
An bayyana cewa masu ibadar da aka ’yantar za a sake haɗa su da iyalansu bayan sun kammala karɓar kulawar lafiya da shawarwari na ƙwararru, domin taimaka musu murmurewa daga raɗaɗin da suka fuskanta a lokacin da suke hannun masu garkuwa da mutane. Wannan nasara ta sake ƙarfafa fatan al’umma kan samun zaman lafiya mai ɗorewa a Jihar Kaduna.
